Saturday, 24 March 2018

KWALLON KAFA.
MOSES YA KAI NIJERIYA GA GACI.
Ranar Juma'a Najeriya ta doke Poland da ci 1-0 a wasan tunkarar gasar cin kofin duniya inda dan wasan Chelsea Victor Moses ya samar mata fanaretin, bayan da aka yi masa keta, ya kuma buga ya ci.
Su ma kasashen Afirka biyu sun yi nasara inda Tunisia ta doke Iran da ci 1-0 yayin da Morocco ta buge Serbia da ci 2-1.
A bangare guda, Senegal ta da Uzbekistan sun tashi da ci 1-1, yayin da Masar ta sha kashi a hannun Portugal da ci 2-1.
http://www.kurna3.blogspot.comhttps//www.kurna3.blogspot.com

No comments: